in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD na sanya ido kan yanayin da ake ciki a DRC bayan zaben kasar
2019-01-11 09:48:03 cri
Mai magana da yawun babban sakataren MDD Stephane Dujarric, ya bayyana cewa, MDDr tana sanya ido kan yanayin da ake ciki a Jamhuriyar demokuradiyar Congo(DRC), yayin da ake farfagabar takaddama kan sakamakon zaben shugabancin kasar na makon da ya gabata da aka sanar ka iya haddasa tashin hankali.

Jami'in ya ce tawagar MDD dake kasar, na ci gaba da bibiyar abubuwan dake faruwa a kasar, ko da yake tawagar ta ce, al'amura na gudana yadda ya kamata a kasar.

Bayan sanar da sakamakon zaben shugabancin kasar na ranar 30 ga watan Disamban shekarar da ta gabata, babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki, da su guji tayar da zaune tsaye, kana su gabatar da duk wani kokensu na zabe ta hanyoyin da doka ta tanada.

Babban sakataren MDDr ya kara nanata kuduri da goyon bayan majalisar na ci gaba da hada kai da masu ruwa da tsaki na shiyya da abokan huldar kasa da kasa, na ganin an samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma ci gaba a kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China