in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya yi jawabi wajen bikin murnar cika shekaru 40 da kulla hulda tsakanin Sin da Amurka
2019-01-10 19:38:35 cri
A yau Alhamis ne aka yi liyafar murnar cika shekaru 40, da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen Sin da Amurka a nan birnin Beijing fadar mulkin kasar Sin, bikin da ya samu halartar mataimakin shugaban kasar Sin Wang Qishan, wanda kuma ya gabatar da jawabi.

A cewar Wang, don kara kyautata huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, kamata ya yi kasashen 2 su tsaya kan manufar samar da dadaito, da hadin kai, da yanayi na kwanciyar hankali don amfanin jama'ar bangarorin 2, gami da ta daukacin duniya baki daya.

Jami'in ya kara da cewa, ra'ayi daya da shugabannin kasashen 2 suka cimma, ya nuna alkiblar da za a nufa, yayin da ake kokarin raya huldar dake tsakanin bangarorin 2. Ya ce wannan huldar ta riga ta zama irinta mafi tasiri a duniya, wadda kuma za a iya kara kyautata ta a nan gaba.

Ban da haka, cikin wadannan shekaru 40, kasashen Sin da Amurka sun haye wahalhalu, suna kuma ta kokarin raya huldar dake tsakaninsu, tare da cimma nasarori sosai. Wadannan nasarori, a cewar jami'in, sun haifar da babbar moriya ga jama'ar bangarorin 2, gami da taimakawa wanzuwar zaman lafiya, da kwanciyar hankali, da kuma zaman walwala a duniyarmu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China