A cewar hukumar Tshisekedi na jam'iyyar UDPS, ya samu yawan kuri'u sama da miliyan 7 daga sassan kasar daban daban, in ban da birane uku da ba a kammala zabe a cikin su ba sakamakon tashe tashen hankula.
Mr. Tshisekedi ya shige gaban dan takarar jam'iyya mai mulkin kasar Martin Fayulu, da kuma dan takarar jam'iyyun hadaka na masu mulkin kasar Emmanuel Ramazani Shadary. (Saminu Hassan)