in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren harkokin wajen Amurka ya kai ziyara a Iraki
2019-01-10 11:20:11 cri
Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ya kai ziyara a birnin Bagdad na kasar Iraki ba zato ba tsammani, inda ya gana da shugabannin sabuwar gwamnatin kasar, da tattauna batutuwan hadin gwiwar yaki da ta'addanci da sauransu.

Ofishin shugaban kasar Iraki ya bayar da sanarwa a wannan rana cewa, shugaban kasar Barham Salih ya bayyana a yayin ganawarsa tare da Pompeo cewa, yana son kara yin hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa da yankuna, da kawar da rashin tabbaci a yankin Larabawa, da warware matsalar ta'addanci da tsattsauran ra'ayi. A nasa bangare, Pompeo ya bayyana cewa, kasar Iraki muhimmiyar abokiyar kasar Amurka ce a fannonin siyasa da tattalin arziki da tsaro, kasar Amurka tana son zuba jari da shiga aikin sake gina kasar Iraki, musamman taimakawa wajen sake gina biranen da aka karbe ikonsu daga hannun kungiyar IS.

Pompeo ya kuma gana da firaministan kasar Iraki Adel Abdul Mahdi da shugaban majalisar dokokin kasar Mohamed al-Halbousi da kuma ministan harkokin wajen kasar Muhammad Ali al-Hakim.

Pompeo ya fara kai ziyara a kasashe 8 na yankin Gabas ta Tsakiya ciki har da kasar Jordan, da Masar, da Saudiyya tun daga ranar 8 ga wannan wata. Bisa shirin kai ziyara da aka tsara, bai kunshi kasar Iraki ba. Majalisar gudanarwar kasar Amurka ta bayyana a ranar 4 ga wata cewa, a yayin ziyarar Pompeo, za a yi alkawari ga kasashen kawacenta cewa, kasar Amurka ba za ta janye daga yankin Gabas ta Tsakiya ba domin tinkarar barazanar kasar Iran tare da su. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China