in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yarjejeniyar tsakaita bude wuta a birnin Hodeidah na Yemen ta samu karbuwa, in ji jami'in MDD
2019-01-10 11:18:06 cri

Gwamnatin kasar Yemen da 'yan tawayen Houthi sun nuna cikakkiyar mutuntawa ga yarjejeniyar tsakaita bude wuta a birnin Hodeidah na kasar, in ji Martin Griffiths, wakilin musamma na MDD kan batun Yemen, wanda ya bayyana hakan a jiya Laraba.

"Ina farin cikin sanar da cewa, dukkan bangarorin sun amince da yarjejeniyar tsakaita bude wutar a Hodeidah, wacce aka amince za ta fara aiki tun a ranar 18 ga watan Disamba, kuma an samu gagarumin ci gaba wajen raguwar tashe tashen hankula tun daga wancen lokaci," Griffiths ya bayyana hakan ne ga kwamitin sulhun MDD.

Ana samun tashe tashen hankula a wasu yankuna, da suka hada da birnin Hodeidah, da kuma wasu yankunan kudancin kasar Yemen. Sai dai kuma, tashe tashen hankula ba su da yawa sosai idan an kwatanta da gabanin lokacin kulla yarjejeniyar a kasar Sweden, in ji shi.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China