in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban majalisar kolin Iran ya ce kasarsa ba za ta mika wuya ga masu karfin fada a ji ba
2019-01-10 11:05:15 cri
Rahotanni daga kamfanin dillancin labaran kasar Iran sun ce, shugaban majalisar kolin kasar Iran Seyyed Ali Khamenei ya gabatar da wani jawabi yayin da yake halartar taron tunawa da juyin juya halin Islama da aka yi a kasar, inda ya jaddada cewa, kasarsa ba za ta mika wuya ga masu karfin fada a ji ba.

Game da batun sake kakabawa Iran takunkumi da Amurka ta yi, Seyyed Ali Khamenei ya ce, mutanen Amurka na ganin cewa takunkumin da aka sanya ya kasance wanda ba'a taba ganin irinsa ba a tarihi, amma ina tabbatar da cewa su ma za su ji kunya wadda ba'a taba ganin irinta ba a tarihi.

Khamenei ya ce, takunkumin da Amurka ta sanyawa Iran yana matsawa kasar gami da al'ummarta lamba, yana bukatar jami'an gwamnatin Iran da su maida hankali kan bangaren zaman rayuwar al'umma, da bada fifiko kan tallafawa mutane masu fama da talauci, tare kuma da inganta kwarewar matasan kasar.

Khamenei ya sake jaddada cewa, ya kamata a kwantar da hankali yayin da ake fuskantar ayyukan da Amurka da Turai suke yi, inda ya ce, barazana da alkawari ko kuma sanya hannun da suka yi duk ba za'a iya yarda da su ba.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China