Shugaban kasar Koriya ta Arewa Kim Jong-un ya kawo ziyara kasar Sin
2019-01-08 10:55:00
cri
Kakakin sashin kula da harkokin kasa da kasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya sanar a yau Talata 8 ga wata a nan birnin Beijing cewa, bisa gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi masa, shugaban jam'iyyar WPK ta kasar Koriya ta Arewa kuma shugaban kasar Kim Jong-un yana ziyara a kasar Sin tun daga ranar 7 zuwa 10 ga wannan wata. (Zainab)