in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojoji sun ayyana kafa majalissar gudanarwa a kasar Gabon
2019-01-07 19:03:38 cri
Dakarun rundunar sojojin kasar Gabon, sun amshe iko da kafar radiyon kasar da sanyin safiyar yau Litinin, inda suka ayyana kafa majalissar gudanarwar ta kasa.

Cikin wata sanarwar da wani jami'in rundunar ya karanta ta kafar Radiyon kasar, sojojin sun zargi shugaban kasar Ali Bongo Ondimba, wanda a yanzu yake jinya a wani asibitin dake kasar Morocco, da gazawa wajen sauke nauyin dake kansa na shugabanci, suna masu cewa, bayanin da ya gabatar domin murnar shiga sabuwar shekara, a ranar 31 ga watan Disambar da ya shude, cike yake da farfaganda ta yunkurin ci gaba da rike madafun iko.

Shugaba Bongo ne shugaban Gabon tun daga shekarar 2009, an kuma sake zabensa a karon karshe a shekarar 2016.

Rahotanni na cewa, sojojin sun shiga farfajiyar gidan radiyon kasar ne da misalin karfe 4 na asubahin Litinin din nan bisa agogon kasar. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China