in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kasar Kamaru sun halaka kwamandoji biyu na mayakan 'yan aware a yankin da ake fama da riikici
2019-01-07 09:24:19 cri
Rahotanni daga kasar Kamaru na cewa sojojin kasar sun yi nasarar kashe kwamandoji biyu na mayakan 'yan aware a yankin kudu maso yammacin kasar, daya daga cikin yankunan kasar da ake magana da T]urancin Ingilsihi da yaki ya wargaza

Rundunar sojojin kasar ta bayyana cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya Lahadi cewa, an kashe janar Obi ne, wadda kungiyarsa ke damun al'ummomin Manfe da Okoyong da Bahuo Ntaida Bachou Akagbe da kua Nchemba ne a safiyar ranar 6 ga watan Janairun shekarar 2019.

A cewar sanarwar, samamen da sojojin bataliyar dake kai daukin gaggawa(BIR) suka kaddamar shi ma ya kai ga halaka janar Eyong, daya daga cikin kwamandojin mayakan 'yan awaren. An kuma lalata sansanoninsu tare da gano ko lalata wasu makamai

Samamen da sojojin suka kaddamar na zuwa ne kimanin mako guda bayan da shugaba Paul Biya na kasar ta Kamaru, ya gargadi mayakan yayin jawabin karshen shekara da ya saba gabatarwa al'ummar kasar, cewa zai sanya kafar wando guda da mayakan muddin suka ki ajiye makamansu don bin hanyar da ta dace.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China