in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An dage bayyana sakamakon babban zaben DRC zuwa makon gobe
2019-01-06 15:27:54 cri
Sakamakon babban zaben da aka gudanar a jamhuriyar demokuradiyyar Kongo (DRC), wanda ake sa ran bayyana shi a yau Lahadi, an dage zuwa makon gobe, kamar yadda Corneille Nangaa, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta na kasar (CENI) ya sanar.

"Ba zai yiwu a sanar da sakamakon zaben a ranar Lahadi ba. Muna dukkan shirye shiryen da suka dace amma har zuwa yanzu ba mu kammala komai da komai ba," in ji Corneille Nangaa, ya sanar da hakan ne a jiya Asabar ba tare da bayyana takamammiyar ranar da za'a sanar da sakamakon zaben ba.

"A makon gobe muke sa ran fitar da sakamakon," in ji shi.

A cewar Nangaa, hukumar zaben ta CENI ta karbi kashi 45 zuwa 48 bisa 100 ne kadai na takardun kada kuri'ar a duk fadin kasar.

A ranar 30 ga watan Disamba ne aka gudanar da babban zaben a fadin kasar, in bada wasu birane 3 wadanda aka dage zaben sakamakon matsalar rashin tsaro gami da barazanar barkewar annobar cutar Ebola, wadda ta yi mummunar barna a yankuna masu yawa na arewacin lardin Kivu dake gabashin kasar ta Kongo. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China