in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu kasashe biyar sun fara zama membobin wucin gadi a kwamitin tsaron MDD
2019-01-03 10:48:25 cri
Tun daga jiya Laraba 2 ga wata, wasu kasashe biyar, ciki har da Jamus, da Jamhuriyar Dominican, da Afirka ta Kudu, da Belgium da kuma Indonsiya sun soma zama membobin da ba na dindindin ba a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

Wa'adin aikin kasashen biyar ya fara ne daga ranar 1 ga watan Janairun bana har zuwa ranar 31 ga watan Disambar shekarar 2020. Sauran wasu kasashe biyar da ba na dindindin ba a kwamitin sulhun sun hada da Poland, da Kwadibwa, da Kuwait, da Peru gami da Equatorial Guinea, wadanda wa'adin aikinsu zai cika a karshen shekarar da muke ciki.

A halin yanzu, kwamitin sulhun MDD na kunshe da membobi 15, ciki har da zaunannun membobi guda biyar, da suka hada da Sin da Faransa da Rasha da Birtaniya gami da Amurka, yayin da sauran wasu kasashe goma wadanda ke zama membobin da ba na dindind ba. Tsawon wa'adin aikin kasashe membobin da ba na dindindin ba shine shekaru biyu, kuma kowace shekara za'a canja guda biyar, amma ba zasu yi tazarce ba. Za'a zabi kasashe membobin da ba na dindindin ba bisa nahiyoyin da suke, wato guda uku daga Afirka, guda biyu-biyu daga yankin Asiya da Pasifik, da na Latin Amurka da yankin Caribbean, da yankin yammacin Turai da sauran wasu yankuna, sa'annan guda daya daga yankin gabashin Turai.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China