in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin kasar Sudan ta tsawaita dokar tabaci a jihohin Kassala da North Kordofan
2019-01-03 10:29:15 cri
A jiya Laraba majalisar dokokin kasar Sudan ta amince da wasu dokokin biyu na shugaban kasar inda ta tsawaita dokar tabaci a jihar Kassala dake gabashin Sudan da kuma jihar North Kordofan dake yammacin kasar ta Sudan, kafar intanet ta Ashorooq ne ta bada rahoton.

Rahoton ya ce, majalisar dokokin kasar ta amince da tsawaita dokar tabaci ne a jihohin kasar biyu zuwa ranar 20 ga watan Yunin shekarar 2019.

Majalisar ta bada hujjar tsawaita wa'adin dokar tabacin ne sakamakon yadda ake samun yawaitar safarar mutane, makamai, da fataucin miyagun kwayoyi da kuma yadda ake kara samun yawaitar makamai a jihar Kassala.

A ranar 30 ga watan Disambar shekarar 2017, shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya ayyana dokar tabaci a jihohin North Kordofan da Kassala. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China