Xi, wanda har ila shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, kana shugaban askarawar kasar, zai gabatar da jawabi yayin taron da zai gudana a babban dakin taron jama'a da misali karfe 10 na safiyar ranar Laraba 2 ga watan Janairun sabuwar shekara
Za kuma a watsa bikin kai tsaye ta kafofin rukunin watsa labarai na China Media Group da shafin intanet na kamfanin dillancin labarai na Xinhua (Xinhua.com). Haka kuma za a watsa bikin kai tsaye ta manyan shafukan watsa labarai ciki har da people.com.cn da cctv.com da china.com.cn da kuma manhajan watsa labarai na jaridar people's Daily, da kamfanin dillancin labarai na Xinhua da babban gidan talabijin na kasar Sin, CCTV. (Ibrahim)