in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha ta kwashe 'yan kasarta sama da 4,000 daga yakin gabas ta tsakiya da kasashen Afrika
2018-12-29 16:54:54 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Habasha (MoFA) ta sanar a jiya Juma'a cewa, ta kwashe 'yan kasarta kimanin 4,168 a cikin makonni 2 da suka shude daga yankin gabas ta tsakiya da kuma kasashen Afrika.

Habasha ta kwashe 'yan kasarta ne daga kasashen Tanzania, Libya da kuma hadaddiyar daular larabawa (UAE).

Da yake jawabi ga 'yan jaridu na ciki da wajen kasar, Meles Alem, kakakin ma'aikatar ta MoFA, yace gwamnatin ta samu nasarar kwashe 'yan kasar ne bisa hadin gwiwa da hukumomin kasashen Tanzanian, Libyan da UAE.

Rahotanni sun ce dubban 'yan kasar Habasha ne ake yin safararsu zuwa kasashen waje a duk shekara.

Masu yin safarar bil adama suna bi ne ta wasu hanyoyi 3, da suka hada da shiyyar arewacin kasar zuwa Sudan, Libya da bahar Rum inda suke tsallakawa Turai.

Hanya ta biyu itace ta gabashin kasar ta hanyar Somalia, Djibouti da tekun Red Sea inda suke tsallakwa zuwa kasar Saudi Arabia.

Hanya ta uku itace ta kudancin kasar ta Kenya, Tanzania da Mozambique inda suke bullewa zuwa kasar Afrika ta kudu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China