in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An dage wa'adin jefa kuri'a a wasu wuraren Congo-Kinshasa
2018-12-27 11:18:32 cri
Bisa labarin da kwamitin kula da harkokin zabe mai zaman kansa na kasar Congo-Kinshasa ya fidda a jiya Laraba, an ce, an jinkirta jefa kuri'u a wasu wurare na shiyyar dake arewa masu gabashi da kuma yammacin kasar, a babban zaben kasar saboda yaduwar cutar Ebola da kuma rikice-rikicen da aka tayar tsakanin kabilu daban daban na wuraren.

A ranar 30 ga watan nan da muke ciki, za a gudanar da zaben shugaban kasa da na mambobin majalisar dokokin kasar da kuma zaben mambobin majalisun dokokin jihohi a kasar ta Congo-Kinshasa.

Kwamitin kula da harkokin zabe mai zaman kansa na kasar ya fidda sanarwa a ranar 26 ga wata cewa, za a jinkirta ayyukan jefa kuri'u a wasu wuraren dake arewa masu gabashi da kuma yammacin kasar zuwa watan Maris na shekara mai zuwa. A sa'i daya kuma, ya ce, za a gabatar da sakamakon babban zaben shugaban kasa a ranar 15 ga watan Janairu na shekarar 2019, sa'an nan, za a rantsar da sabon shugaban kasa a ranar 18 ga watan Janairu na shekarar 2019. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China