in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha tana neman saukaka ayyukan masu zuba jari a kasar
2018-12-27 10:43:45 cri
Gwamnatin kasar Habasha, a jiya Laraba, ta kaddamar da wani shirin kyautata muhallin zuba jari a kasar, ta hanyar samar da karin damammaki ga 'yan kasuwa na kasashen waje.

Wannan sabon shirin ya kunshi wasu ayyuka fiye da 80, wadanda suka shafi hukumomin kasar guda 10.

Yayin sanar da wannan shirin, ofishin firaministan kasar Abiy Ahmed ya bayyana cewa, shirin zai zama karkashin sa idon sashi mai kula da tsara manufofi da gudanar da su na ofishin firaministan kasar, tare da hadin gwiwar hukumar zuba jari ta kasar EIC.

A cewar firaministan, sabon shirin shi ne wani bangare na babban shirin kasar na samar da karin guraben aikin yi. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China