in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha ta cafke jami'ai sama da 50 bisa zarginsu da hannu a rashawa
2018-12-26 10:45:58 cri
A jiya Talata kasar Habasha ta sanar da cewa ta kama wasu jami'an gwamnatin 56 a yakin da take yi da cin hanci da rashawa.

Jami'an gwamnatin 56 suna aiki ne a yankin jahar Oromia na kasar, yankin wanda ke shiyyar tsakiyar kasar, ana zarginsu ne da rashin tafiyar da ayyukansu bisa ka'ida da kuma yin almubazzaranci da dukiyar gwamnati, kafar yada labarai ta yankin Oromia (OBN) ne ta bada rahoton.

Hukumar yaki da rashawa ta yankin Oromia tana shirin sake damke wasu jami'an nan da wasu kwanaki masu zuwa, in ji OBN.

A watan Nuwamba, kasar Habasha ta kama wasu manyan jami'an sojojin kasar, wadanda take zarginsu da hannu a ayyukan cin hanci da rashawa.

Kama mutanen, yana daga cikin muhimman matakan yaki da rashawa da cin zarafin bil adama, kuma yana daga cikin muhimman alkawurran da gwamnatin sabon firaiministan kasar Ahmed Abey ta yi ga al'ummar kasar, tun bayan nada shi a mukamin firaiministan a watan Afrilun wannan shekara. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China