Zai fara kamfen dinsa daga garin Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom. Babban mai ba shugaban kasa shawara a kan harkokin majalisa, Sanata Ita Enang ne ya bayyana hakan a ranar Litinin 24 ga watan Disamba yayin da yake jawabi ga manema labarai a Uyo.
Enang ya bayyana cewa shugaban kasa zai kasance a jihar tare da shugaban jam'iyyar na kasa Kwamrad Adams Oshiomhole da kuma babban jigon jam'iyyar. Ya kuma bayyana cewa jam'iyyar za ta yi amfani da damar wajen gabatar da tutar jam'iyyar ga 'yan takarar gwamna na APC a jihohin Akwa Ibom, Cross River da Delta. (Leadership A Yau)