in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata kasa da kasa su kara sauraren ra'ayin kasashen Afirka yayin da suke yin hadin-gwiwa da su
2018-12-25 19:35:22 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Hua Chunying ta bayyana yau Talata cewa, yayin da kasashen duniya ke gudanar da hadin-gwiwa tare da kasashen Afirka, kamata ya yi su kara sauraren ra'ayoyinsu, da amincewa da hikimominsu, gami da girmama niyyarsu.

Rahotannin sun ce, yayin da shugaban kasar Rwanda Paul Kagame ke zantawa da kafofin watsa labarai kwanakin baya a Vienna, babban birnin kasar Austria, ya ce, mu'amalar dake tsakanin Sin da Afirka abu ne mai kyau. Ya ce Sin na nuna himma da kwazo wajen gudanar da ayyukan hadin-gwiwa a Rwanda amma ta hanyar da ta dace. Kagame ya ce, kasashen Afirka sun san karfin da suke da shi, da kuma wadanne irin shawarwari ne ya kamata su amince da su daga kasar Sin, don haka ba za su tsunduma cikin basusuka masu tarin yawa ba.

Shugaba Kagame ya kara da cewa, wannan ya danganta da mutanen Afirka, su ne kuma suka san yaya za su yi hadin-gwiwa tare da kasar Sin. Haka kuma, irin rashin gaskiya da wasu Turawa suke nunawa ya ba shi mamaki sosai.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China