in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta kalubalanci wasu kasashe da su girmama mulkin kan shari'arta
2018-12-25 10:39:13 cri
Game da matakin da kasar Canada ta dauka na neman goyon bayan kasashe kawacenta don nuna damuwa kan tsare mutanen kasarta guda biyu da kasar Sin ke yi, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta ce, Sin ta nuna rashin jin dadi da adawa kan wasu magungunan da wasu kasashe, ciki har da Canada da Amurka da dai sauransu suka yi, kuma ta kalubalanci wasu kasashen da batun ya shafa su nuna girmamawa kan mulkin kan shari'a na kasar Sin.

Madam Hua ta bayyana haka ne a yayin taron manema labaru da aka shirya a jiya Litinin, inda ta ce, jama'ar kasar Canada Michael Kovrig da Michael Spavor sun aikata laifukan kawo illa ga tsaron kasar Sin, ko shakka babu hukumomin da abun ya shafa na kasar Sin su dauki matakai masu tsanani kan su bisa doka.

Game da damuwar da kasar Burtaniya da kungiyar EU suka nuna kan mutanen biyu da ake tsere da su a makon da ya wuce, madam Hua ta ce, a hakika dai sun dauki ma'auni biyu kan hakkin bil Adama. Da ma kasar Canada ta tsare babbar jami'ar wani kamfanin kasar Sin bisa bukatar kasar Amurka, wadda har ma kasar Canada ta amince da cewa ba ta sabawa kowace irin doka ba, wannan mataki shi ne ainihin aikin tsarewa ba bisa doka ba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China