Abdullahi Bule, mai gabatar da kara a kotun, ya gayawa manema labaru hakan a jiya Litinin. Ya ce, kotun ta tabbatar da laifin dan kungiyar al-Shabab din mai suna Abdulkadir Abubakar, bisa yadda ya taka muhimmiyar rawa a wasu jerin hare-haren bom da aka kai birnin Mogadishu, cikinsu har da wani da aka kai hotel din Wehliye a watan Maris na bara, wanda ya kashe mutane 10, da jikkatar wasu 17.
Jami'in ya ce, an kama mutumin ne yayin da yake tuka wata mota mai dauke da boma-bomai a yankin Hamarwayne, a watan Mayun shekarar 2017. Tun daga lokacin, kotun ta riga ta yi zama har karo 3 don tantance laifin da mutumin ya aikata. (Bello Wang)