in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta ba da tallafi ga aikin ceto a Indonesia
2018-12-24 20:37:01 cri
Wasu rahotanni na cewa, ya zuwa yanzu a kalla mutane 281 ne suka rasu, yayin da wasu 1016 suka jikkata, sakamakon aukuwar murdawar igiyar ruwan teku mai karfin gaske ta tsunami, a mashigin tekun Sund dake yammacin Indonesia a daren ranar 22 ga wata.

Game da haka, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin madam Hua Chunying, ta ce kasar Sin za ta samar da tallafi ga kasar Indonesia a fannin aikin ceton da ake yi game da wannan bala'in, ta hanyar kungiyar agaji ta red cross da dai sauransu.

Hua Chunying ta bayyana hakan ne, yayin taron manema labaru da aka shirya a yau Litinin. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China