in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran ya ce jibge sojojinta da Amurka ta yi a yankin Gabas ta Tsakiya kuskure ne
2018-12-24 11:32:12 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran Bahram Qassemi ya maida martani game da batun janye sojojinta daga kasar Siriya da gwamnatin Amurka za ta yi, inda ya ce, jibge sojojin da Amurka ta yi a yankin Gabas ta Tsakiya wani babban kuskure ne tun farkon farawa, wanda ya kasance daya daga cikin muhimman dalilan da suka jawo rashin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Bahram Qassemi ya bayyana cewa, girke sojoji a yankin Gabas ta Tsakiya wani mataki ne da gwamnatin Amurka ta dauka bisa kuskure da rashin tunani, wanda kuma ya haddasa rikici a yankin. Bahram Qassemi ya ce, idan aka dubi yanayin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya, za'a iya gano cewa, jibge sojojin Amurka a wajen ya tsananta halin da ake ciki gami da haifar da tashe-tashen hankali, kuma sam bai yi tasiri mai kyau ba.

Rahotannin da aka ruwaito sun ce, shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa za'a janye sojojin kasarsa daga kasar Siriya nan bada jimawa ba, al'amarin da ya haddasa neman yin murabus din ministan tsaron kasar Amurkar, James Mattis. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China