in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taron kolin ECOWAS ba tare da baiwa Morocco lasisin shiga kungiyar ba
2018-12-23 15:40:33 cri
A jiya Asabar aka kammala taron kungiyar raya ci gaban tattalin arzikin kasashen Afrika ta yamma (ECOWAS) a birnin tarayyar Najeriya Abuja, ba tare da an tabo batun baiwa kasar Morocco damar shiga cikin kungiyar ba, kasancewar batun ba ya daga cikin ajandodin taron kolin kungiyar na wannan karo.

An yi tsammanin taron shugabannin kasashen kungiyar ta ECOWAS karo na 54 zai cimma matsaya wajen amincewar shigar kasar Morocco kungiyar.

Kasar Morocco ta gabatar da bukatar neman zaman mamba ta ECOWAS ne bayan da ta koma kungiyar tarayyar Afrika a watan Janairun shekarar 2017. An amince da kasar ta zama mambar AU ne a lokacin taron kolin ECOWAS a watan Yunin shekarar 2017, wanda ya gudana a Monrovia, babban birnin kasar Liberia.

An gabatar da bincike game da tasirin kasar na zama mamba a kungiyar daga bisani aka gabatarwa shugabannin kungiyar kasashen yammacin Afrika a taron kolin kungiyar karo na 52, wanda aka gudanar a watan Disambar 2017 a Abuja, inda shugabannin suka gaza cimma matsaya kan batun.

A halin yanzu, ECOWAS tana da mambobin kasashen yammacin Afrika 15, daga cikinsu babu wata kasa da ta hada kan iyaka da kasar Morocco, kasar wacce ke shiyyar arewacin Afrika. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China