in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci a tallafawa zaben 'yan majalisar dokokin Guinea-Bissau
2018-12-22 16:14:37 cri
A jiya Juma'a wani wakilin kasar Sin ya bukaci kasa da kasa su samar da tallafin kwararru, da kudade da kuma na kayan aiki don gudanar da zaben 'yan majalisar dokokin kasar Guinea-Bissau.

"Muna fata dukkannin bangarorin da abin ya shafa a Guinea-Bissau za su yi aiki tare domin tabbatar da ganin an gudanar da zaben cikin lumana kamar yadda aka tsara gudanarwa," inji Wu Haitao, mataimakain zaunannen wakilin kasar Sin a MDD. Ya bayyana hakan ne a taron kwamitin sulhun MDDr.

Zaben 'yan majalisar dokokin kasar ta Guinea-Bissau da farko an shirya gudanar da shi ne a ranar 18 ga watan Nuwamba, amma an dage shi sakamakon matsalar kalubalolin rashin kwararru. Sai dai shugaban kasar ta yammacin Afrika Jose Mario Vaz, a ranar Alhamsi ya fitar da wata doka, inda ya ayyana ranar 10 ga watan Mayun shekarar 2019 a matsayin sabuwar ranar gudanar da zaben kasar.

Wajibi ne alummomin kasashen duniya su kiyaye ikon mallaka da 'yancin cin gashin kai da martabar kasar ta Guinea-Bissau, inji Wu, ya kara da cewa, kasar Sin za ta yi aiki da sauran kasashen duniya wajen ci gaba da tattaunawa tsakanin dukkannin bangarorin da basa ga maciji da juna a Guinea-Bissau, domin tabbatar da samun dawwamamman zaman lafiya da kuma cigaban kasar ta yammacin Afrika baki daya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China