in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin jakadancin Sin ya musanta zargin da kafafen yada labaran Canada suka yi kan satar bayanai
2018-12-22 15:40:25 cri
Zarge zargen da kafar yada labaran kasar Canada ta yiwa kasar Sin game da satar bayanai labarai ne na karya, wanda ya yi matukar jefa al'umma cin rudani, ofishin jakadancin kasar Sin a birnin Ottawa na kasar Canada shi ne ya bayyana hakan a ranar Juma'a.

Kafar yada labaran kasar Canada a kwanan nan ta ba da rahotanni dake cewa hukumomin Amurka suna tuhumar wasu 'yan kasar Sin biyu inda ake zarginsu da satar bayanai ta kafar intanet.

Rahotannin sun kuma zargi kasar Sin da laifin yin kutse a kafar intanet ta kasar Canada, kana sun zargi kasar ta Sin da cewa ta saba alkawarin da ta dauka na kin yin amfani da kafar intanet wajen satar wasu bayanan sirri da suka shafi harkokin kasuwanci da fasahohi mallakin kamfanoni masu zaman kansu na kasar Canada.

"Kasar Sin ba ta taba daukar nauyin yin kutse a kafofin intanet na kasar Canada ba, ballanta ma ta ce wai za ta dakatar da duk wasu batutuwa dake da alaka da hakan. Wani ba zai yi alkawarin dakatar da abin da bai aikata ba," in ji sanarwar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China