in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da taron aikin tattalin arziki na kwamitin tsakiyar jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin a Beijing
2018-12-21 19:26:34 cri
Tun daga ranar 12 zuwa yau 19 ga watan da muke ciki, an gudanar da taron aikin tattalin arziki na kwamitin tsakiyar jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin a Beijing, fadar mulkin kasar Sin, taron da ya samu halartar shugaban kasar Sin Xi Jinping, da firaministan kasar Li Keqiang, da sauran manyan kusoshin kasar.

A jawabin da ya gabatar yayin taron, shugaba Xi ya zayyana ayyukan tattalin arzikin kasar Sin a shekarar 2018, sannan ya yi tsokaci kan yanayin da tattalin arzikin duniya ke ciki, kana ya gabatar da shirin ayyukan da za a gudanar a shekara mai zuwa.

Shugabannin kasar Sin da suka halarci taron sun tabbatar da wasu manyan ayyukan da za a lura da su a shekarar 2019, wadanda suka hada da: raya masana'antu mai inganci, da habaka kasuwannin cikin gida, da raya kauyuka da yankunan karkara, da neman samun daidaito tsakanin shiyyoyi daban daban, da kara kokarin gyara tsarin tattalin arziki, da bude kofa ga kasashen waje daga dukkan fannoni, gami da kara kyautata zaman rayuwar jama'ar kasar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China