in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ware dala miliyan 10 don dakile annobar Ebola a tsakiyar Afrika
2018-12-13 09:44:13 cri
Babban jami'in sashen kula da jin kai da daukin gaggawa na MDD Mark Lowcock ya sanar a jiya Laraba cewa an ware dalar Amurka miliyan 10 domin gudanar da aikin dakile annobar cutar Ebola a tsakiyar Afrika.

Wata sanarwar da hukumar ta fitar ta ce kudaden wanda babban sashen bada agajin gaggawa na MDD wato (CERF) ya samar da su, za'a yi amfani da kudaden wajen daukar matakan dakile yiwuwar barkewar annobar Ebola domin hana cutar bazuwa a kasashen dake makwabtaka da jamhuriyar demokaradiyyar Kongo (DRC).

"Hukumomin kai daukin gaggawa, wadanda hukumar lafiya ta duniya (WHO) ke jagoranta, suna yin aiki tukuru wajen ganin an dakile bazuwar annobar cutar ta Ebola a gabashin DRC, amma abu ne mai matukar muhimmanci a tallafawa kasashen dake makwabtaka da Kongon. Samar da kudade a kan lokaci da hukumar CERF ta yi yana da muhimmanci, hakan zai yi matukar tasiri wajen hana kwayoyin cutar yaduwa a makwabtan kasashe," in ji Lowcock. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China