in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
CIIE zai gayyaci karin mahalarta a 2019
2018-12-12 15:50:11 cri
Labarin Jaridar China Daily ta ruwaito cewa, bayan nasarar gudanar da baje kolin kayakin da ake shigo da su kasar Sin na farko CIIE, mashiryansa sun aike da wakilai kasashen waje, domin jan hankali karin mahalarta a taron na shekarar 2019 da za a yi a birnin Shanghai.

Jaridar ta ce an tura manyan jami'ai karkashin jagorancin Liu Fuxue, mataimakin shugaban hukumar kula da CIIE, zuwa kasashen Australia da New Zealand, domin gayyato 'yan kasuwar wuraren.

Liu Fuxue, ya ce tun daga watan Yulin bana aka fara rejistar baje kolin na badi, kuma akwai bukatar wadanda ke sha'awar zuwa su yi rejista kafin 30 ga watan Afrilun 2019.

Liu ya kara da cewa, kimanin kamfanoni 100 ne suka rattaba hannu kan kwangiloli tsakaninsu da hukumar kula da CIIE, inda kuma ake ci gaba da tattaunawa game da wasu karin kwangilolin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China