in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha: Amurka na yunkurin wankewa dakaru masu adawa da gwamnatin Syria daga laifin da suka aikata
2018-12-08 17:25:55 cri
Ma'aikatar tsaron kasar Rasha ta bayar da sanarwa a jiya Juma'a cewa, kasar Amurka na yunkurin wankewa dakaru masu adawa da gwamnatin kasar Syria daga laifin da suka aikata na kai farmaki da makamai masu guba a arewacin Syria.

Sanarwar ta ce, ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta ce, harin da aka kai da makamai masu guba da aka kaddamar a karshen watan Nuwamba na bana a Aleppo dake arewacin kasar Syria, ba dakaru masu adawa da gwamnatin Syria ne suka yi ba, sai dai sojojin gwamnatin Syria ne suka yi amfani da barkonon tsohuwa. Kasar Amurka ta yi wannan bayani ne da nufin wankewa dakaru masu adawa da gwamnatin Syria daga laifin da suka aikata, da kuma sanya kasashen duniya su rage maida hankali kan boma-boman da kasar Amurka ta harba a gabashin kasar Syria, wadanda suka haddasa rasuwar fararen hula da rautata wasu.

Kafofin watsa labaru na Syria sun bayar da labari a ranar 24 ga watan Nuwamba cewa, dakaru masu adawa da gwamnatin sun yi amfani da makaman roka masu guba don kai farmaki kan matsugunai da tituna na Aleppo, wannan ya sanya wasu fararen hula da dama suka kasa numfashi, ciki har da mata da yara. Bayan faruwar lamarin, sojojin gwamnatin kasar sun mayar da martani kan wurin da dakaru masu adawa da gwamnatin suka harba makaman roka. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China