in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan Afrika ta kudu za su rika sintiri a asibitoci domin dakile aukuwar hare-hare
2018-12-07 11:22:36 cri

Ma'aikatar lafiya ta kasar Afrika ta kudu ta ce la'akari da hare-haren da ake kai wa jami'an lafiya a baya-bayan nan a wasu asibitoci a kasar, za a tura 'yan sanda su rika sintiri a wasu daga cikin asibitoci domin kiyaye tsaro.

Kakakin ma'aikatar Popo Maja, ya ce a wannan lokaci na bukukuwa, an ba su tabbacin 'yan sanda za su taimakawa wajen yin sintiri a wasu muhimman asibitoci, musammam ma a wuraren da ake fi samun riginginmu.

An kai wa likitoci 3 na asibitin Letaba dake Limpopo hari makonni kadan da suka gabata. Inda ake zargin wata tawagar masu dauke da makamai da ta ci karfin jami'an dake gadi, da raunata likitocin.

A cewar Popo Maja, su na zargin harin ya samo asali ne daga laifukan da ake aikatawa wanda ba za a lamunta ba, kuma a don haka ne 'yan sanda suka ce za su kara sintirin da suke yi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China