in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi fashin baki game da tasirin matakan ci gaba wajen wanzar da zaman lafiya
2018-12-06 09:18:43 cri
Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya ce aiwatar da matakan samar da ci gaba, na da ma'anar gaske a fannin wanzar da zaman lafiya, musamman a kasashe ko yankunan dake farfadowa bayan fuskantar tashe tashen hankula.

Ma Zhaoxu ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, yayin mahawarar da kwamitin tsaron MDD ya gudanar. Ya ce akwai bukatar dora muhimmancin gaske a fannonin samar da ci gaba, da tsaro, da yaki da fatara, matsalolin da akasarinsu ne ke haifar da tashe tashen hankula a sassan duniya.

Kaza lika jami'in ya yi kira ga kasashen duniya da su rika sauke nauyin dake wuyan su, na aiwatar da ajandar MDD ta wanzar da ci gaba mai dorewa nan da shekarar 2030, yana mai jaddada bukatar hadin gwiwa domin samar da ci gaba, da karrama ayyukan tallafi, domin wanzar da zaman lafiya yadda ya kamata. Jami'in ya yi nuni ga tasirin manufar MDD ta shekarar 2015, wadda ta tanaji aiwatar da wasu kudurorin ci gaba 17 nan da shekarar 2030.

Har ila yau, wakilin na Sin ya ja hankalin kasashen duniya, da su tallafawa kasashe masu yunkurin farfadowa bayan fuskantar tashe tashen hankula da dabarun aiwatar da manufofin su, bisa yanayi da kuma ikon su na aiwatar da matakai bisa radin kan su. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China