in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya gana da shugabar majalisar dokokin jama'ar kasar Panama
2018-12-04 10:30:22 cri
A ranar 3 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugabar majalisar dokokin jama'ar kasar Panama Yanibel Ábrego a birnin Panama dake kasar.

A yayin ganawar, Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin tana son yin kokari tare da kasar Panama, wajen sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa tushen ka'idar Sin daya tak, ya kuma yi imanin cewa, za a kiyaye hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu har abada.

A nata bangare, Ábrego ta bayyana cewa, jam'iyyun kasar Panama sun cimma daidaito, da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Panama da Sin, wanda hakan ya samar da dama ga hadin gwiwar kasashen biyu. Ta ce majalissar dokokin jama'ar kasar Panama tana son kara yin mu'amala tare da kasar Sin, wajen samar da gudummawar inganta hadin gwiwarsu, da sada zumunta a tsakaninsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China