in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Peng Liyuan ta gana da uwargidan shugaban kasar Panama
2018-12-04 10:04:01 cri
A ranar 3 ga wata da tsakar rana, uwargidan shugaban kasar Sin kuma wakiliyar hukumar WTO mai kula da magance da yaki da cutar AIDS, kuma wakiliyar musamman ta hukumar bada ilmi da kimiyya da al'adu ta MDD mai kula da bada ilmi ga mata da yara mata Peng Liyuan, ta gana da uwargidan shugaban kasar Panama, kuma wakiliyar musamman ta hukumar shirin kula da cutar AIDS ta MDD dake yankin Latin Amurka, kuma shugabar majalisar kula da harkokin kananan yara ta kasar Panama Lorena Castillo Garcia de Varela, a fadar shugaban kasar Panama, tare da halartar bikin fadakarwa da magance da yaki da cutar AIDS tare.

Peng Liyuan ta bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin ta dora muhimmanci sosai kan ayyukan magancewa, da yaki da cutar AIDS, da kula da masu dauke da cutar, ta samun wasu nasarori a wannan fanni. Kana kasar Sin ta nuna yabo ga kasar Panama, bisa kokarinta a wannan fanni. Ta ce Sin ta maida hankali ga ayyukan dake shafar mata da yara, da yin kokari wajen inganta karfin bada ilmi, da tabbatar da kiwon lafiya ga mata da yara. Ta kuma yi fatan Sin da Panama za su kara samar da gudummawa wajen raya sha'anin mata da yara na kasashen biyu, har ma da na duk duniya gaba daya.

A nata bangare, Castillo ta nuna yabo ga gwamnatin kasar Sin, bisa samun nasarori da ta samu wajen magancewa, da yaki da cutar AIDS, da tabbatar da hakkin mata da yara. Ta ce kasarta za ta ci gaba da yin kokari tare da kasar Sin, wajen sa kaimi ga kara samun nasarori a wadannan fannoni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China