Kasar Sin ta yi imanin cewa, muddin kasashe membobin kungiyar G20 su ka yi shawawari da juna sa'an nan su ka cimma ra'ayi daya, da daukar nauyin dake wuyansu bisa ra'ayin raya makomar bil'adama ta bai daya, da kuma karfafa hadin-gwiwa tsakaninsu, ko shakka babu za su bayar da karin gudummawa ga ci gaban tattalin arzikin duniya da kyautatuwar zaman rayuwar al'ummomin duniya. Kasar Sin ita ma za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa a wannan fanni.(Murtala Zhang)