SANA ya tabbatar da aukuwar wannan hari na yammacin jiya Lahadi, sai dai kuma ya ce ba a samu asarar rayuka yayin harin ba. Harin dai na makamai masu linzami, an yi nufin ya sauka kan wani sansani na sojojin dake lardin na Homs, to sai dai babu wasu cikakkun bayanai daga tsagin gwamnatin kasar game da aukuwar sa.
A wani ci gaban kuma, wani tsagi na masu fafutuka dake kasar ya bayyana cewa, an kaddamar da harin ne kan wani ayari na sojojin gwamnatin Syria a kusa da hamadar Homs, bisa kusantar da suka yiwa sansanin Amurka dake yankin. (Saminu Hassan)