Shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya yi kira da a dauki karin matakan karfafa bunkasa aikin dasa itatuwa masu kare rairayi a arewacin kasar sa. Shugaba Xi ya ce akwai bukatar shafe tsawon lokaci ana daukar matakai, da gudanar da kirkire kirkire, wadanda za su karfafa, da gina tattalin arziki a wannan yanki na kasar.
Xi ya gabatar da kiran ne, yayin da ya yi jawabi game da aikin gina shingen gandayen daji uku a yankin Arewacin kasar.(Saminu Alhassan)