in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira ga kasashen duniya da su kiyaye tsarin cinikayya cikin 'yanci da kasancewar bangarori daban-daban
2018-11-30 09:53:23 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin cinikayyar kasar Sin Gao Feng, ya yi kira ga kasashe mambobin kungiyar G20, da su hada kai wajen ganin sun kirkiro tsarin tattalin arzikin mai salon bude kofa ga kowa, da inganttacen sakamakon tattalin arzikin da cinikayya yayin taron kolin kungiyar na G20 da zai gudana a kasar Argentina.

Ya ce, yanzu zamani ne na dunkulewar tattalin arzikin duniya waje guda, don haka ya kamata a yi kokarin kare tsarin cinikayya cikin 'yanci da kasancewar bangarori daban-daban.

Gao Feng ya ce, karuwar ra'ayin ba da kariya ga harkokin cinikayya da ra'ayin kashin kai, sun haifar da rashin tabbas ga ci gaban tattalin arzikin duniya, lamarin dake bukatar hadin gwiwar dukkan bangarori.

Ya ce, kasar Sin na fatan hada kai da kasar Argetina da ma ragowar sassa wajen zurfafa alaka a fannonin cinikayya da zuba jari, da bude kofar kasuwanni da samar da sabbin damammakin bunkasuwa.

Bayanai na nuna cewa, alkaluman GDPn mambobin G20 ya kai kaso 86 cikin 100 na GDPn duniya, yayin da darajar cinikyayyarsu ta kai kimanin kaso 80 cikin 100 na darajar cinikayyar duniya baki daya.

A don haka, jami'in na kasar Sin ya ce kasarsa na fatan yin sahihiyar tattaunawa da dukkan mambobin kungiyar game da harkokin cinikayyar kasa da kasa da sauran batutuwa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China