Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin ta yi Allah wadai da kakkausar murya kan duk wasu hare-haren da ake kai wa hukumomin diplomasiyya. Jami'in na bayyana hakan ne, yayin da yake yiwa manema labarai karin haske kan harin da aka kai wa karamin ofishin jakadancin Sin dake birnin Karachi na kasar Pakistan
Jami'in ya kara da cewa, daukacin ma'aikatan dake aiki a karamin ofishin jadakanci da daukacin iyalansu suna cikin koshin lafiya a halin yanzu, kana gwamnatin kasar Sin ta nuna juyayi ga jami'an tsaron kasar Pakistan wadanda suka rasa rayukansu a yayin harin, haka kuma ta isar da sakon jaje ga iyalan jami'an tsaron da sauran wadanda suka ji rauni a harin.(Jamila)