Ana sa ran cibiyar ta CACS mai jami'ai da malamai, ta taka muhimmiyar rawa wajen tattara bayanai da bitar ci gaban dangantakar Sin da Afrika.
A cewar David Monyae, Daraktan cibiyar, kuma daya daga cikin daraktocin kwalejin Confucius dake Jami'ar ta Johannesburg, ana samun bayanai na karya game da dangantakar Sin da Afrika ne saboda rashin sahihan bayanai ga al'umma.
Ya ce cibiyar za ta mayar da hankali kan dangantakar Sin da Afrika, da kuma auna tasirin manyan ayyukan samar da ababen more rayuwa a Afrika, ciki har da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da zamanantar da ayyukan masana'antu da musaya tsakanin jama'ar bangarorin biyu da kuma alakar bangarorin. (Fa'iza Mustapha)