Sanarwar ta ce, sojojin Amurka sun hada gwiwa da sojojin gwamnatin Somaliya, wadanda suka kai hare-haren sama har sau biyu ga sansanin kungiyar al-Shabaab da ke tsakiyar kasar Somaliya.
Sanarwar ta kara da cewa, sojojin Amurka za ta ci gaba da hada gwiwa da tawagar musamman da tarayyar Afirka ta tura zuwa Somaliya, da kuma rundunar tsaro ta Somaliya don yakar 'yan ta'adda.
Kungiyar Al-shabaab, kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ce da ke da nasaba da kungiyar al-Qaeda, wadda ta sha kai hare-hare a Somaliya, da ma kasashen da ke makwabtaka da ita. (Lubabatu)