in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Staffan de Mistura ya alkawarta kaimi ga kafuwar kwamitin samar da kundin mulki a Syria
2018-11-20 11:10:15 cri
Wakili na musamman ga babban magatakardar MDD game da kasar Syria Staffan de Mistura, ya ce zai yiwa sassan masu ruwa da tsaki kaimi, bisa burin da ake da shi, na kafa kwamitin da zai tsara kundin mulkin kasar ta Syria.

Staffan de Mistura ya bayyana hakan ne ta kafar talabijin daga birnin Geneva, ga zauren kwamitin tsaron MDD a jiya Litinin, yana mai cewa fatansa shi ne kafin karshen watan Disamba mai kamawa, za a kai ga gudanar da zama na farko na wannan kwamiti.

Bisa ka'ida wa'adin aikin Staffan de Mistura zai kammala ne a karshen watan nan, amma ya ce zai ci gaba da zama kan mukamin sa, har ya zuwa wata mai zuwa domin yin hobbasa na karshe, domin cimma burin kafuwar wannan kwamiti. Jami'in ya kara da cewa, MDD ta shirya tsaf, domin ba da dukkanin gudummawa ta kafuwar kwamitin, ko da yake dai bai kore yuwar gamuwa da cikas a aikin da ake yi a yanzu ba.

A jawabin sa na karshen cikin wata mai zuwa ga zauren kwamitin tsaron MDD, de Mistura zai yi karin haske, game da inda aka tsaya a aikin kafuwar kwamitin tsara kundin mulkin kasar ta Syria.

Babban magatakardar Antonio Guterres ya riga ya bayyana sunan Geir Pedersen daga kasar Norway, a matsayin wanda zai maye gurbin de Mistura. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China