in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
PLO: kudurin Amurka na Allah wadai da kungiyar Hamas jirkita gaskiya ne
2018-11-19 11:10:49 cri
Babban sakataren kwamitin koli na kungiyar dake fafutukar 'yantar da al'ummar Falasdinawa ta PLO Saeb Erekat, ya yi kira ga kasashen duniya, da su yi tir da matakan da shugaba Donald Trump na Amurka ke dauka, game da rikicin Falasdinawa da yahudawan Isra'ila.

Erekat ya ce kudurin Amurka na yin Allah wadai da matakan da Hamas ke dauka a zirin gaza, jirkita tsagwaron gaskiya ne. Wata sanarwar da jami'in na PLO ya fitar, yayin wani taron manema labarai, ta yi tofin Allah-tsine, game da kudurin na Amurka, wanda ke kira ga MDD da ta yi tir da ayyukan Hamas. Amurkan dai ta ce Hamas na haifar da tashe tashen hankula, tare da harba makaman roka cikin yankunan Isra'ila.

Mr. Erekat ya kara da cewa, Isra'ilan ce ya kamata ta dauki alhakin dukkanin abubuwan dake faruwa a yankin, duba da yadda take ci gaba da mamayar matsugunan Falasdinu, tana kuma kafa shingaye, da hallaka fararen hula, da tsare mutane, da kuma aikata kisan kiyashi.

Daga nan sai ya yi kira ga kungiyar Hamas wadda ke iko da zirin Gaza, da ta gaggauta amincewa da yunkurin kasar Masar, na kau da baraka tsakanin abokan tafiyar ta, tare da cimma burin hadin kai da sulhu. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China