in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu ya yi Allah-wadai da kisan dakarun wanzar da zaman lafiya a DRC
2018-11-16 12:55:30 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya yi Allah-wadai da kisan a kalla sojoji 20 yayin da suke aikin tabbatar da zaman lafiya a yankin gabashin Jamhuriyar demokirdiyyar Congo(DRC).

A cikin wata sanarwa da kwamitin ya fitar, mambobin kwamitin sun mika sakon ta'aziya ga iyalan wadanda aka kashe ciki har da dakarun wanzar da zaman lafiya 7 daga kasar Malawi da guda daga Tanzaniya da kuma a kalla sojoji 12 'yan kasar ta DRC, tare da fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.

A ranar Larabar da ta gabata ce dai aka kashe sojojin, yayin da suke kai hare-haren hadin gwiwa karkashin laimar MDD wato MONUSCO da sojojin Jamhuriyar demokiradiyar Congo a kan dakarun kungiyar 'yan tawayen ADF a DRC da Uganda da yankin Beni dake arewacin Kivu.

Mambobin kwamitin sulhun sun kuma bayyana goyon bayansu ga dakarun kasashen Malawi da Tanzaniya, wadanda ke ci gaba da aiki a yanayi mai wahalar gaske a kokarin da suke yi na kare mazauna wuraren daga hare-haren mayakan na ADF da sauran kungiyoyi masu dauke da makamai.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China