in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatan kwastam na kasar Sin sun damke mutane 17 da ake zargi da sumugan haurin giwa
2018-11-16 12:40:18 cri
Ma'aikatan kwastan a yankin Shenzhen dake kasar Sin sun damke wasu mutane 17 da ake zargi da sumogan haurin giwa daga Afirka da nauyinsa ya kai kilomgram 323.7

A cikin mutanen 17 da aka damke, akwai mazauna yankin Hong Kong guda shida, wadanda suka yi yunkurin shigo da haurin giwa babban yankin kasar Sin ta hanyar Hong Kong.

Tuni a watan Yulin shekarar 2017 da ta gabata ce, aka kama irin wadansu mutanen da ake zarginsu da fasa kwaurin haurin giwa. An dai kafa wata tawagar hadin gwiwa, karkashin babbar hukumar kwastam ta kasar, domin ta kara gudanar da bincike game da lamarin.

Tawagar ta kuma kai samame biyu, wanda ya kai ta ga damke wadanda ake zargin a watannin Yuni da kuma Yuli. An yi kiyasin cewa, bata garin sun yi sumogan kusan kilogram dubu na haurin giwa da wasu kayayyaki dake da nasaba da sassan dabbobi tun a watan Nuwamban shekarar 2017.

A shekarar 2015 ne dai gwamnatin kasar Sin ta dakatar da shigo da haurin giwa da dukkan kayayyakin masu alaka da shi, ta kuma dakatar da sarrafawa da ma sayar da haurin giwa baki daya a karshen shekarar 2017.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China