Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Najeriya ko ICPC a takaice ta ce za ta binciki zargin karbar na goro da ake yiwa shugaban jam'iyyar APC mai mulkin kasar Adams Oshiomhole a lokacin zaben fidda 'yan takarar jam'iyyar da aka kammala ba da dadewa ba.
Mai magana da yawun hukumar Rasheedat Okoduwa ita ce ta bayyana hakan ga manema labarai a Abuja, fadar mulkin kasar.
Shawarar da hukumar ICPC ta yanke ta bincikar shugaban na APC na zuwa ne mako guda bayan da 'yan sandan farin kaya na kasar suka tuhume shi bisa zargin yin ba dai-dai ba a zaben fidda 'yan takarar jam'iyyar, inda aka bukace shi da ya sauka daga mukaminsa.(Ibrahim)