Kasar Sin ta bude wani katafaren bikin yau Talata a nan birnin Beijing, domin bikin cika shekaru 40 da fara aiwatar da manufarta ta bude kofa ga kasashen waje da gyare-gyare a cikin gida.
Zaunannen mamba a hukumar kula da harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na JKS, kuma mamba a sakatariyar kwamitin tsakiya na jam'iyyar, Wang Huning ne ya ayyana bude bikin a gidan adana kayayyakin tarihi na kasar Sin da safiyar yau Talata. (Fa'iza Msutapha)