in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi musayar munanan hare-hare tsakanin Yankin Gaza da Isra'ila
2018-11-13 10:59:51 cri

Sojojin Isra'ila, sun kaddamar da luguden wuta kan zirin Gaza da yammacin jiya Litinin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 3 da raunata wasu gommai, a wani martani da suka mayar ga rokokin da aka harba masu daga zirin.

Kakakin ma'aikatar lafiya ta Gaza, Ashraf al-Qedra, ya shaidawa manema labarai cewa, an gano mutane 3 da suka mutu, wadanda suka hada da Mohamed al-Tatari mai shekaru 27 da Mohamed Oudeh mai shekaru 22 da kuma Hammad al-Nahal mai shekaru 23.

Wani ganau ya ce jiragen yakin Isra'ila sun auna wani gida ne dake garin Rafa na kudancin zirin Gaza.

Wata gajeriyar sanarwa da kawacen kungiyar mayakan Falasdinu, ciki har da Hamas ta fitar, ta tabbatar da aukuwar hare-haren, inda ta ce dakarun kungiyar sun harba rokoki daga zirin Gaza zuwa matsugunan 'yan adawa da yammacin jiya Littinin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China