in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Trump ya bukaci kada Saudiyya da kungiyar OPEC su rage man da suke samarwa
2018-11-13 10:31:28 cri
Shugaban Amurka Donald Trump, ya bukaci Saudiyya da kungiyar kasashen dake samar da man fetur OPEC, kada su rage yawan man da suke samarwa.

Donald Trump ya wallafa a shafinsa na Tweeter a jiya cewa, yana fatan Saudiyya da OPEC ba za su rage samar da mai ba, kuma kamata ya yi farashin mai ya yi kasa bisa yadda ake samarwa.

Hukumar kula da makamashi ta Amurka, ta bayyana a watan da ya gabata cewa, dawo da takunkumai kan Iran da Amurka ta yi, zai kara haifar da rashin tabbas kan farashin man fetur, kuma tasirin takunkuman zai karu a nan kusa.

Daga bisani ne kuma, OPEC ta ce kasashe mambobinta, sun shiryawa cimma bukatun kasuwar mai ta duniya, ko da za a samu karancin mai saboda dalilai na siyasa, sannan za su ci gaba da kokarin tabbatar da daidaito a kasuwar mai.

Dangantakar Amurka da Saudiyya ta dan samu tangarda a baya bayan nan, sanadiyyar yawan mutanen da hare-haren da Saudiyyar ke jagoranta ya rutsa da su a Yemen da kuma kisan dan jaridar kasar Jamal Khashoggi a Turkiyya. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China