in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar kawancen Larabawa ta bukaci bangarorin Libya sun cimma matsayar siyasa
2018-11-12 10:25:50 cri
Sakatare Janar na kungiyar kawancen Larabawa, Ahmed Aboul-Geit, ya bukaci bangarori masu rikici a Libya, su cimma matsaya kan tsarin siyasa da kundin tsarin mulki da dokokin zabe, kamar yadda al'ummar kasar ke muradi.

Wata sanarwar da kakakin kungiyar Mahmoud Afifi ya fitar, ta ruwaito Ahmed Aboul-Geit na kira ga jam'iyyun siyasa a kasar, su shawo kan takkadamar dake tsakaninsu da rarrabuwar kawuna a kasar da yaki ya daidaita.

Ya kuma bayyana fatan al'ummar kasar za su cimma yarjejeniyar da za ta kai ga gudanar da zabuka karkashin sahihan dokoki da kundin tsarin mulki.

Duk da jam'iyyun siyasar kasar sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da MDD ta dauki nauyi a shekarar 2015, har yanzu Libya na fuskantar takkadama tsakanin gwamnatocin dake gabashi da yammacin kasar, inda dukaninsu ke fafutukar samun halacci. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China